Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kadan Daga Duniyar Tamaula


Mai horas da mai tsaron raga na kungiyar kwallon Kafa ta AS Roma Claudio Tafferal ya bayyana cewar mai tsaron ragar kungiyar Alisson mai shekaru 25 da haihuwa na jin dadin zamansa a kungiyar don haka babu inda zai koma, a yanzu duk da kasancewar kungiyar Liverpool ta matsa kaimi wajan ganin ta saye shi a kakar wasan bana.

Kungiyar kwallon Kafa ta Paris Saint-Germain ta bayyana sha'awarta ta ganin ta dauko dan wasan tsakiya na Chelsea N'Golo Kante, dan shekaru 27 da haihuwa wanda wikilansa suka gana da daraktan wasanni na kungiyar.

Inter Milan tana zawarcin dan wasan baya na kungiyar Chelsea, mai suna Davide Zappacosta, dan shekaru 26 a duniya.

Kungiyar kwallon Kafa ta Arsenal, tana dab da kammala cinikin dan wasan baya na tsakiya mai suna Caglar Soyuncu, mai shekaru 22 da haihuwa daga kungiyar kwallon Kafa ta Freiburg, dake kasar jamus tuni dai wakilin dan wasan ya tabbatar da cewar tattaunawa ta yi nisa kan batun.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:10 0:00

  • 16x9 Image

    Ibrahim Jarmai

    Ibrahim Jarmai, ma’aikacin jarida (International Broadcaster Multi Media) a sashen Hausa na muryar Amurka, mai gabatar da shirye shirye a radio da talabijin, da kuma shafukan yanar gizo, dan asalin jihar Kasina.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG