Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Jaddawalin Wasannin Share Fagen Cin Kofin Duniya


A cigaba da wasannin sada zumunta da ake yi tsakanin kasa da kasa domin shirye shiryen tunkarar gasar cin kofin kwallon kafa na duniya da za a yi a watan yuni 2018 a can kasar Rasha.

A jiya kasar Brazil ta doke Croatia daci 2-1

Albania 1-4 Ukraine,

Costa Rica, ta lallasa Northern Ireland daci 3-0

Spain nada 1 Switzerland 1,

Mexico 1-0 Scotland,

Saudi Arabia ta sha kashi daci 3-0 a hannun Peru.

A yau kuma kasar India zasu fafata da kasar Kenya, Armenia da Moldova, Serbia da Chile, Morocco zasu barje gumi da Slovakia, sai kuma kasar Itali su kara da kasar Malta.

Za a fara wasannin ne tun daga misalin karfe 3 da rabi na yammaci har zuwa takwas saura kwata na yamma agogon Najeriya Nijar Kamaru da kasar Kenya Ghana.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:52 0:00

  • 16x9 Image

    Bala Branco

    Bala Branco ma'aikacin jarida ne a Albarka Radio FM Bauchi dake tarayyan Najeriya wanda yake shirya wa Dandalin VOA labaran wasanni, Haifaffen Unguwar Nufawa ne dake birnin Bauchi. Mazaunin Bauchi a Najeriya.

  • 16x9 Image

    Ibrahim Jarmai

    Ibrahim Jarmai, ma’aikacin jarida (International Broadcaster Multi Media) a sashen Hausa na muryar Amurka, mai gabatar da shirye shirye a radio da talabijin, da kuma shafukan yanar gizo, dan asalin jihar Kasina.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG