Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Yau Za'a Fafata A Wasannin Copa Del Rey 2016/2017


A cigaba da wasannin Copa Del Rey na shekarar 2016/17, na kasar Spain, yau za'a kece raini tsakanin Kungiyoyin kwallon kafa guda goma.

Kungiyar kwallon kafa ta Villarreal, zata karbi bakuncin Toledo

Las, Palmas, zata fafata tsakaninta da Kungiyar kwallon kafa ta Huesca, ita kuwa Real Sociedad zata kece raini da kungiyar Real Valladolid.

Malaga zata marabci Cordoba, daga karshe Atletico Madrid, zasu fafata da kungiyar kwallon kafa ta Guijuelo.

Za'a buga wasanninne a lokuta daban daban agogon Najeriya Nijar kamaru da kasar Chadi.

Har ila yau jiya an buga wasa daya tilo da ya rage a bangaren Laliga 2016/2017 mako na Goma Sha shida

Athletic Club ta doke Celta vigo da kwallaye 2-1.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:24 0:00


  • 16x9 Image

    Bala Branco

    Bala Branco ma'aikacin jarida ne a Albarka Radio FM Bauchi dake tarayyan Najeriya wanda yake shirya wa Dandalin VOA labaran wasanni, Haifaffen Unguwar Nufawa ne dake birnin Bauchi. Mazaunin Bauchi a Najeriya.

  • 16x9 Image

    Ibrahim Jarmai

    Ibrahim Jarmai, ma’aikacin jarida (International Broadcaster Multi Media) a sashen Hausa na muryar Amurka, mai gabatar da shirye shirye a radio da talabijin, da kuma shafukan yanar gizo, dan asalin jihar Kasina.

XS
SM
MD
LG