Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Wasu 'Yan Jarida Sun Boye Fuskokin Su Wajan Zanga Zanga


Gungun wasu ‘yan jarida dauke da kwalaye sun saka bakaken ledoji a fuskokinsu, sun yi zanga zanga a jihar Geogia ta kasar Amurka, domin nuna rashin amincewarsu akan sacewa da garkame wani dan jaridar kasar Afganistan me suna Mukhtari.

Lauyan Mukhtari, ya bayyana cewa an sace dan jaridar mai zaman kansa ne daga jihar Geogia, inda aka tafi da shi Azerbaijan.

Lauyan ya bayyana cewa wadanda suka sace Mukhtar na sanye ne da kaya irin na jami’an ‘yan sandan Giogia, lauyan ya kuma yi ikirarin cewa an sa tukwicin kudi Euro dubu goma akan duk wanda ya sace shi da kuma ketara iyakar kasar Amurka da shi ta barauniyar hanya ya kuma kai Mukhtari.

Gwamnatin Amurka da hukumomin tarayyar Turai da kuma kungiyoyin kare hakkin bil’adama na kasa da kasa sun bukaci shugabannin jihar Giogia su gudanar da bincike a kan lamarin.

  • 16x9 Image

    Ibrahim Jarmai

    Ibrahim Jarmai, ma’aikacin jarida (International Broadcaster Multi Media) a sashen Hausa na muryar Amurka, mai gabatar da shirye shirye a radio da talabijin, da kuma shafukan yanar gizo, dan asalin jihar Kasina.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG