Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Tosin Kehinde Ya Yanke Shawarar Taka Leda A Kungiyar Super Eagles


Matashin dan kwallon nan na kungiyar kwallon kafa ta Manchester United, Tosin Kehinde ya yanke shawarar buga wa Najeriya, wasa a matakin kasa da kasa.

Dan wasan mai shekarun haihuwa 19, wanda ya cancanci buga wasa a Ingila, an nuna hotunansa yana gaisawa da mai horas da kungiyar Super Eagles na Najeriya, Gernot Rohr a wasan da suka buga a London tare da Serbia, a makon da ya wuce kuma ya tabbatar da cewa ya zabi Super Eagles a matsayin kungiyar sa.

Ya kuma ce Najeriya, ta kasance wani ɓangare na san a musamman. Kehinde ya shaida wa kafar sadarwar BBC. "An haife ni a can, ‘yan uwana duka na Najeriya ne. Na fito ne daga wata zuriya mai karfi a Najeriya”.

Kehinde ya samu shiga atisaye da manyan ‘yan wasn Manchester United, a karon farko a kakar wasa ta bana kuma ya buga wasanni 15 a ‘yan kasa da shekaru 23 na Manchester united.

Har ila yau Wani matashin dan wasan Chelsea wanda ba a bayyana sunan sa ba a Ingila zai iya kasancewa a tawagar ‘yan wasan Najeriya, a nan gaba.

An ce dan wasan ya fara tattaunawar sirri tare da jami'an kula da wasa na kasa a hotel a London kafin wasan Najeriya da Serbia, wanda ya gudana a satin da ya gabata.

  • 16x9 Image

    Ibrahim Jarmai

    Ibrahim Jarmai, ma’aikacin jarida (International Broadcaster Multi Media) a sashen Hausa na muryar Amurka, mai gabatar da shirye shirye a radio da talabijin, da kuma shafukan yanar gizo, dan asalin jihar Kasina.

  • 16x9 Image

    Bala Branco

    Bala Branco ma'aikacin jarida ne a Albarka Radio FM Bauchi dake tarayyan Najeriya wanda yake shirya wa Dandalin VOA labaran wasanni, Haifaffen Unguwar Nufawa ne dake birnin Bauchi. Mazaunin Bauchi a Najeriya.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG