Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Hukumar FIFA Zata Binciki Zargin Wariyar Launin Fata Akan Pogba Da Dembele


Hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA zata dubi gaskiyar abinda ya faru na nuna wariyar launin fata a wasan da Faransa ta samu nasara a kan Rasha da kwallaye 3-1 a wasan sada zumunta da akayi a cikin makon nan

Hukumar kula da wasan na duniya ta ce a cikin wata sanarwa da suka samu sun "tattara rahotanni daban-daban da ke shaida mai yiwuwa" na nuna bambanci ga dan wasan.

Manchester United, Paul Pogba da kuma ​Ousmane Dembele, na Barcelona.

Tawagar ‘yan wasan kwallon Kafa na mata na kungiyar Chelsea ta kai ga wasan kusa da na karshe na gasar zakarun Turai bangaren mata a karon farko bayan ta doke Montpellier da ci 3-1 da ci 2--0 a gida wanda hakan ya bata jimillar kwallaye 5-1.

Itama tawagar mata ta Manchester City ta kai ga wasan Kusa da na karshe dukkan kungiyoyi biyu na Ingila suna nuni da cewa akwai kulob din Burtaniya biyu a cikin' wasan kusa da na karshe a karo na farko a tarihin wasan bangaren mata.

Chelsea da Wolfsburg zasu hadu a wasan dab da na karshe sai kuma Manchester City da Lyon masu rike da kofin.

Dan kwallon Leicester City, Kelechi Iheanacho bai fafata a wasan sada zumunta da kasar Serbia, ta doke Najeriya da ci 2 -0 sakamakon karayar kashi a hannunsa a ranar Talata, kocin Super Eagles Gernot Rohr ya bada tabbacin hakan. Kungiyar Leicester ta na shirin duba shi kafin ranar Asabar dazata fafata da Brighton a gasar Firimiya lig na kasar Ingila.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:35 0:00

  • 16x9 Image

    Ibrahim Jarmai

    Ibrahim Jarmai, ma’aikacin jarida (International Broadcaster Multi Media) a sashen Hausa na muryar Amurka, mai gabatar da shirye shirye a radio da talabijin, da kuma shafukan yanar gizo, dan asalin jihar Kasina.

  • 16x9 Image

    Bala Branco

    Bala Branco ma'aikacin jarida ne a Albarka Radio FM Bauchi dake tarayyan Najeriya wanda yake shirya wa Dandalin VOA labaran wasanni, Haifaffen Unguwar Nufawa ne dake birnin Bauchi. Mazaunin Bauchi a Najeriya.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG