Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Bangaren Saye Da Sayarwa Na ‘Yan Wasan Kwallon Kafa


Dan wasan gaba na Everton Wayne Rooney, ya fara tattaunawa da mahukuntan kungiyar Kwallon Kafa ta DC United, dake kasar Amurka kan batun komawarsa kulob din da taka leda a bana.

Manchester United, tana dab da kammala sayen dan wasan tsakiya na kungiyar Shakhtar Donestk, mai suna Fred, wanda ta ce tana da karfin guiwar za'a kammala cinikin nan da sati mai zuwa.

Manchester City, zata biya fam miliyan £60 wajan ganin ta cimma dogon burinta na sayen dan wasan gefe na Leicester City, Riyad Mahrez, wanda tun a watan janairu ta ke kokarin ganin ta kawo shi kulob din ta.

  • 16x9 Image

    Ibrahim Jarmai

    Ibrahim Jarmai, ma’aikacin jarida (International Broadcaster Multi Media) a sashen Hausa na muryar Amurka, mai gabatar da shirye shirye a radio da talabijin, da kuma shafukan yanar gizo, dan asalin jihar Kasina.

  • 16x9 Image

    Bala Branco

    Bala Branco ma'aikacin jarida ne a Albarka Radio FM Bauchi dake tarayyan Najeriya wanda yake shirya wa Dandalin VOA labaran wasanni, Haifaffen Unguwar Nufawa ne dake birnin Bauchi. Mazaunin Bauchi a Najeriya.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG