Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Hukumar UEFA Na Tuhumar Kungiyar Atletico Madrid


Hukumar dake kula da wasan kwallon Kafa ta nahiyar turai Uefa ta na tuhumar kungiyar kwallon Kafa ta Atletico Madrid ta kasar Spain, bisa zarginta da nuna wariyar launin fata a wasan da suka buga na karshe na cin kofin Europe League na shekarar 2017/18 a ranar talata 16/5/2018 tsakanita da Olympicos Marseille inda ta samu nasarar lashe gasar bayan ta doke Marseille da kwallaye 3-0.

Uefa ta ce magoya bayan Atletico Madrid, sun daga kyalle mai dauke da rubutun da yake nuna wariyar launi haka kuma sun yi kunna wuta tare da jefa wasu abubuwa cikin fili yayin wasan wanda yin haka ya saba wa dokokin hukumar.

Don haka hukumar ta ce kwamintin ladaftarwa na Uefa zai yi zama akan wannan alamarin ranar 31 ga watan Mayu 2018 domin daukar mataki game da lamarin.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:09 0:00

  • 16x9 Image

    Ibrahim Jarmai

    Ibrahim Jarmai, ma’aikacin jarida (International Broadcaster Multi Media) a sashen Hausa na muryar Amurka, mai gabatar da shirye shirye a radio da talabijin, da kuma shafukan yanar gizo, dan asalin jihar Kasina.

  • 16x9 Image

    Bala Branco

    Bala Branco ma'aikacin jarida ne a Albarka Radio FM Bauchi dake tarayyan Najeriya wanda yake shirya wa Dandalin VOA labaran wasanni, Haifaffen Unguwar Nufawa ne dake birnin Bauchi. Mazaunin Bauchi a Najeriya.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG