Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Labaran Duniyar Tamaula Da Dumi-Dumin Su


Kasar Ingila ta bayyana sunan dan wasan gaba na kungiyar kwallon Kafa ta Tottenham, Harry Kane, a matsayin Kaftin din kungiyar kwallon Kafa ta Ingila.

Dan wasan zai jagoranci ‘yan wasan Ingila a gasar cin kofin duniya da za a yi a kasar Rasha, a bana 2018.

Harry Kane, me shekaru 24 da haihuwa ya zurara kwallaye 41 a dukkan wasannin da ya buga na shekarar da ta gabata inda kungiyar Tottenham ta kammala a mataki na uku a gasar Firimiya lig 2017/18 ta kasar Ingila.

Ya kuma taimaka wa kasarsa ta Ingila wajan samun tikitin shiga gasar cin kofin duniya da za'ayi musamman a wasansu da kasar Scotland, wanda suka tashi 2-2 dan wasan shi ya jefa kwallo da aka tashi hakan a mintocin karshe wanda haka ya bata damar hayewa.

Kane, ya zurara kwallaye 12 a wasanni 23 da ya buga wa kasarsa ta Ingila.

Kocin kasar Ingila Southgate, ya ce dama a cikin ‘yan wasa biyu ne yake so ya zabi daya daga ciki ya zamo Kaftin a kungiyar da Henderson, na Liverpool. da kuma Harry Kane. Amman daga bisani ya yanke shawarar bai wa Harry Kane.

Kasar Ingila dai zata fafata da Najeriya a wasan sada zumunci ranar 2 ga watan yuni 2018, a shirye shiryensu na zuwa gasar cin kofin duniya inda zasu fara bugawa wasansu na rukuni tsakaninsu da Kasar Tunisiya ranar 18 ga watan Yuni.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:03 0:00

  • 16x9 Image

    Ibrahim Jarmai

    Ibrahim Jarmai, ma’aikacin jarida (International Broadcaster Multi Media) a sashen Hausa na muryar Amurka, mai gabatar da shirye shirye a radio da talabijin, da kuma shafukan yanar gizo, dan asalin jihar Kasina.

  • 16x9 Image

    Bala Branco

    Bala Branco ma'aikacin jarida ne a Albarka Radio FM Bauchi dake tarayyan Najeriya wanda yake shirya wa Dandalin VOA labaran wasanni, Haifaffen Unguwar Nufawa ne dake birnin Bauchi. Mazaunin Bauchi a Najeriya.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG