Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Me Ya Yi Zafi Antonio Conte Zai Tattara Komatsansa?


Antonio Conte
Antonio Conte

Kocin kungiyar kwallon Kafa ta Manchester City, Pep Guardiola, na shirin sayen dan wasan tsakiya na Chelsea, Eden Hazard, mai shekaru 27 da haihuwa akan kudi fam miliyan 100.

Kocin kungiyar kwallon Kafa ta Chelsea, Antonio Conte, na shirin barin matsayin sa a kungiyar nan da awoyi 48, inda aka sanya sunan tsohon Kocin Barcelona, Luis Enrique, a cikin jerin wadanda ake ganin zasu maye gurbin Conte a kungiyar.

Manchester United, ta cimma wata yarjejeniya na wucin gadi tsakanita da kungiyar kwallon Kafa ta Benfica, kan dan wasan tsakiyarta mai suna Talisca, wanda yanzu haka yake zaman aro a kungiyar Besiktas.

Kocin Manchester United Jose Mourinho, ya rufe shafinsa na sada zumunci Instagram, sakamakon sakonnin da ake turo masa kan zarginsa da ake yi na rashin samun nasara da Manchester united, bata yi ba a wasan karshe na cin kofin kalu bale (FA Cup) 2017/18 tsakaninta da Chelsea. ranar asabar da ta gabata 19/5/2018, inda aka doke Manchester united da kwallo1- 0.

Saurari cikakken labarin a nan.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:54 0:00

  • 16x9 Image

    Ibrahim Jarmai

    Ibrahim Jarmai, ma’aikacin jarida (International Broadcaster Multi Media) a sashen Hausa na muryar Amurka, mai gabatar da shirye shirye a radio da talabijin, da kuma shafukan yanar gizo, dan asalin jihar Kasina.

  • 16x9 Image

    Bala Branco

    Bala Branco ma'aikacin jarida ne a Albarka Radio FM Bauchi dake tarayyan Najeriya wanda yake shirya wa Dandalin VOA labaran wasanni, Haifaffen Unguwar Nufawa ne dake birnin Bauchi. Mazaunin Bauchi a Najeriya.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG