Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Neymar Zai Iya Zamantowa Zakakarn Kwallon Kafa A Duniya Nan Gaba


Germany Soccer Champions League Final
Germany Soccer Champions League Final

Dan kwallon kasar Kamaru, Samuel Eto’o yayi hasashen cewa dan tamaula na kasar Brazil, Neymar, shine zai zamo zakaran kwallon kafa a duniya nan gaba a bayan Lionel Messi da Cristiano Ronaldo sun gama yayinsu.

Neymar ya jefa kwallaye 70 a raga a wasanni 134 da ya buga ma FC Barcelona tun komawarsa kulob din daga Santos ta Brazil a 2013.

Dan wasan na gaba, ya shiga cikin wadanda suka yi takarar kambun zakaran kwallon kafa na duniya a bayan da ya taimakawa kulob dinsa wajen lashe dukkan manyuan kofuna 3 da ta yi takararsu a shekarar da ta shige.

Eto’o ya fadawa gidan telebijin na ESPN Brazil cewa Neymar na iya zamowa dan kwallon kafa fiye da kowa a duniya. Yace a bayan Messi da Ronaldo sun gama yayinsu, lallai Neymar zai zamo na daya a duniya.

Sai dai kuma, y ace “ya kamata Neymar ya san cewa kusan komai ya dogara ne a kansa. Ya kamata ya san cewa yana da basirar kwallon kafa, amma dole ne ya rika furatis a koyaushe. Ba kowa ne ke da irin basirarsa ta kwallo ba.”

Yaci gaba da cewa “Shekarun Neymar 24 ne kawai, na grime shi da shekaru 10, amma ana daukarsa a zaman jagora a kasar Brazil. A saboda irin basira da kwarewarsa, zai iya bada shawara gad an wasa mai shekaru 35 da suke buga kwallo tare.”

XS
SM
MD
LG