Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Jaddawalin Rukunin Zagaye Na Biyu Na Gasar Cin Kofin Zakarun Nahiyar Turai


A yau talata za'a dawo cigaba da fafatawa a wasan kwallon kafa bangaren gasar cin kofin zakarun Nahiyar Turai, UEFA Champions League, na shekarar 2017/18 a matakin wasan rukunin zagaye na biyu.

A yau kungiyoyi goma sha shida zasu kece raini a tsakaninsu, daga rukuni hudu kamar haka;

A rukunin (E)

Sevilla zata karbi bakuncin Liverpool, sai Spartak Moscow su kara da Maribor,

A rukunin (F)

Manchester City zata barje gumi da Feyenoord, sai kuma Napoli ta fafata da Shakhtar Donestk,

Sai kuma rukunin (G) inda Monaco zasu marabci RB Leipzig, sai Besiktas da FC Porto,

A rukunin (H) kuwa

Apoel Nicosia zasu karbi bakuncin masu riki da kambun Turai Real Madrid, sai a kara tsakanin Borussia Dortmund da kungiyar Tottenham,

Za'a buga wadannan wasanni ne da misalin karfe tara saura kwata na dare agogon Najeriya, Nijar, Kamaru da Kasar Chadi.

please wait

No media source currently available

0:00 0:01:57 0:00

  • 16x9 Image

    Ibrahim Jarmai

    Ibrahim Jarmai, ma’aikacin jarida (International Broadcaster Multi Media) a sashen Hausa na muryar Amurka, mai gabatar da shirye shirye a radio da talabijin, da kuma shafukan yanar gizo, dan asalin jihar Kasina.

  • 16x9 Image

    Bala Branco

    Bala Branco ma'aikacin jarida ne a Albarka Radio FM Bauchi dake tarayyan Najeriya wanda yake shirya wa Dandalin VOA labaran wasanni, Haifaffen Unguwar Nufawa ne dake birnin Bauchi. Mazaunin Bauchi a Najeriya.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG