Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shirin Hallaka Beraye Domin Samun Kudi A Jihar Legas


A kokarin yaki da kawar da Zazzabin nan mai saurin kisa wanda ake dauka daga bera mai suna Lasa, wata kungiya mai zaman kanta karkashin hadin gwiwa da gwamnatin jihar Legas zasu kaddamar da wani sabon shirin hallaka beraye da suka yiwa lakabi da “Ku Kashe beraye Ku samu Kudi.”

A karkashin wannan sabon shirinne kungiyar zata kara azamar amfani da wani sinadari domin hallaka berayen dake ciki da wajen birnin wanda zai taimaka wajan kare jama’a daga kamuwa da kwayoyin cutar ka iya harbar jama’a koda ya rube.

Babban shugaban kamfanin Mr Oluwasegun ya bayyanawa kamfanin dillancin labaran Najeriya cewa shirin zai taimaka wajan kawar da beraye daga jihar.

Kungiyar ga hadin gwiwar gwamnatin jiha na yunkurin kawar da yiwuwar barkewar annobar zazzabin Lasa ta dalilin haka ne suka bullo da shirin sayen matattun beraye akan kudin da ba’a kayyade ba tukuna.

  • 16x9 Image

    Ibrahim Jarmai

    Ibrahim Jarmai, ma’aikacin jarida (International Broadcaster Multi Media) a sashen Hausa na muryar Amurka, mai gabatar da shirye shirye a radio da talabijin, da kuma shafukan yanar gizo, dan asalin jihar Kasina.

XS
SM
MD
LG