Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Wakokin Jan Hankalin Matasa Kan Muguwar Dabi'a - Mahdi Danko


Mahdi Danko
Mahdi Danko

Na kan yi wakokin fadakarwa kuma mussaman na fi maida hankali a bangaren dabi’ar rayuwar samari da ‘yan mata dangane da yadda rayuwa ta canza, kwadayi ya fi yawa a harkar soyayyar matasa inji matashin mawaki Mahdi Danko.

Mahdi Danko, ya bayyana cewa a wata wakarsa da yayiwa lakabi da “A bi sannu” ya ja hankalin matasa akan yadda wasu samari ke amfani da matsala ta talauci ko ta kwadayin abin duniya su lalata ‘yan mata da wasu dabi’u marasa kyau da ba na malam Bahaushe ba.

Ya ce matsalar matsin rayuwa ya haddasa wasu iyayen basa iya kula da iyalinsu yadda ya kamata, kuma mafi yawan lokutan ‘yan mata sai suyi amfani da rashin da iyayensu ke fama da shi su rika bin samari domin samun kudin kashewa ba tare da iyaye sun yi li’akari da daga ina ‘ya’yan su suka samo kudi.

Ya kara da cewa a yanzu a cikin kimanin matasa kaso 10, cikin dari, samari uku ne kadai zasu iya kamewa ba tare da sun saba hanya ba wajen cutar da ‘yan matan su da wasu dabi’u wala Allah na kudi da aikata alfasha ko shigar da su hanyoyin shaye shaye.

Sabanin sauran mawakan da suke yankin Kanon Dabo a wannan karo Mahdi Danko, yayin zantawar sa da wakiliyar dandalinvoa, manajansa mai suna Hamza Hassan Inuwa wanda aka fi sani da Hamza planner, ya ce sun dauki wannan tsari ne domin dauke masa matsalolin da zai iya fuskanta daga bangaren al’umma gudun kada hakan ta shafi harkarsa ta waka.

please wait

No media source currently available

0:00 0:07:29 0:00

  • 16x9 Image

    Ibrahim Jarmai

    Ibrahim Jarmai, ma’aikacin jarida (International Broadcaster Multi Media) a sashen Hausa na muryar Amurka, mai gabatar da shirye shirye a radio da talabijin, da kuma shafukan yanar gizo, dan asalin jihar Kasina.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG