Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugaban Laberiya Geoge Weah Ya Taka Ledar Minti 79


Shugaban kasar Liberia George Weah, ya bugawa kasarsa wasan kwallon kafa a ranar Talata 10/9/2018 yana da shekaru 52, Weah, shine dan kwallon Afirka na farko da ya lashe Kyautar gwarzon dan wasan kwallon kwallon kafa ta duniya FIFA, ya fafata wasanne har na tsawon mintuna 79 a wasan da Najeriya ta yi nasara da ci 2-1 a Monrovia.

Kasar Laberiya ta shirya wannan wasan na sada zumunci don janye riga mai lamba 14, wadda Weah yake sawa a yayin da yake taka leda.

Najeriya ta zuba ‘yan kwallo sosai, ciki har da Wilfred Ndidi na Leicester da dan wasan tsakiya Peter Etebo na Stoke City da Ndidi, Kelechi Iheanacho, wanda suka zo a matsayin canji.

Weah, Tsohon dan wasan AC Milan, da Monaco, Paris St-Germain da Chelsea da kuma Manchester city, ya ajiye takalman wasansa tun shekaru 16 baya, lamarin da ya ba magoya bayan kasar mamaki ganin yadda ya buga wasan da Najeriya, ba tare da wata matsala ba har na tsawon mintuna 79.

An rantsaer da George Weah, a matsayin shugaban kasar laberiya a watan 2018 Janairu.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:45 0:00

  • 16x9 Image

    Ibrahim Jarmai

    Ibrahim Jarmai, ma’aikacin jarida (International Broadcaster Multi Media) a sashen Hausa na muryar Amurka, mai gabatar da shirye shirye a radio da talabijin, da kuma shafukan yanar gizo, dan asalin jihar Kasina.

  • 16x9 Image

    Bala Branco

    Bala Branco ma'aikacin jarida ne a Albarka Radio FM Bauchi dake tarayyan Najeriya wanda yake shirya wa Dandalin VOA labaran wasanni, Haifaffen Unguwar Nufawa ne dake birnin Bauchi. Mazaunin Bauchi a Najeriya.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG