Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugaba Ali Bango Zai Raba Wa Matasa Gadon Sa


Shugaba Ali Bongo na kasar Gabon yace zai mika dukkan kudin da ya gada daga mahaifinsa, tsohon shugaba Omar Bongo, ga wata gidauniyar matasa da za a kafa musamman domin matasan kasar, yayin da zai kuma mika wani ginin dake Libreville babban birnin kasar domin gina jami’a.

A bayan wadannan kuma har ila yau, akwai wasu kadarori guda biyu na marigayi Omar Bongo dake Paris, babban birnin Faransa wadanda su ma za a bayar da su ga kasar.

A lokacin da yake jawabi na bukin cikar shekaru 55 da samun ‘yancin kan kasar Gabon, shugaba Bongo yace a idanunsa, duk ‘yan kasar magadan marigayi shugaba Omar Bongo ne.

Wannan mataki na shugaba Ali Bongo, yana zuwa a daidai lokacin da alkalai a kasar Faransa suke ci gaba da binciken iyalan marigayi Omar Bongo bisa zargin yin rub da ciki a kan dukiyar kasarsu, zargin da suka ce atafau bah aka ba ne.

An yi shekara da shekaru ana zargin marigayi Omar Bongo da laifin handama, inda a shekarar 2010, Faransa ta kaddamar da wani bincike kan satar dukiyar gwamnati bisa matsin lamba daga kungiyoyi irinsu Transparency International.

Har yanzu dai ba a aiwatar da wasiyyar marigayin ba, wanda yam utu a shekarar 2009, bayan yayi mulkin shekaru 41 a kasar Gabon. An ce ya bar dukiya ta miliyoyin dalolin Amurka.

  • 16x9 Image

    Ibrahim Jarmai

    Ibrahim Jarmai, ma’aikacin jarida (International Broadcaster Multi Media) a sashen Hausa na muryar Amurka, mai gabatar da shirye shirye a radio da talabijin, da kuma shafukan yanar gizo, dan asalin jihar Kasina.

XS
SM
MD
LG