Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Fara Kokowar Gargajiya A Kasar Nijar


 Kokowa a Jamhuriyar Nijar
Kokowa a Jamhuriyar Nijar

Ministan matasa, wasannin motsa jikin da al'adu na kasar Nijar, Malam Kasim Mukhtar, ya kaddamar da buda shagulgulan kokowar gargajiya karo na talatin da tara, (39) a Damagaram, inda ‘yan kokowa na jihojin jamhuriyar Nijar, za su kara har tsawon kwanaki goma don samun zakaran da zai dauko takobi.

Mauduin da aka dauka a bana shine gudurmawar matasa a tsarin farfado da kasar Nijar, wanda al’adu na taka mahimmin rawa a cikinsa.

Yahaya Muhammad shugaban kwamitin tsara kokowar ya ce a bana jama’a zasu ga kokowa mai ban sha’awa kuma cikin kyakkyawan tsaro da kuma wani sabon tsari na saka kokowar nakasassu a ciki a bana domin suma a dama dasu.

Ya kara da cewa za a tabbatar da ganin cewa an magance kura kuran da suka faru a baya domin cigaban kokowa a kasar Nijar.

A kokowar ta yau Dosso ta kara da Diffa Maradi da Tillaberi, Dosso ta tashi da kaye shida Diffa kaye uku mutuwar kasko daya.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:24 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG