Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Amfanin Ilimi Ba Dan Aiki Kadai Ba Ko Dan Tarbiyantar Da 'Ya'Ya


Amina Bello Suleman
Amina Bello Suleman

Matsalar da na fara fuskanta kasancewar ina karanta aikin jiyya shine kalmomin da ban saba jin suba sakamakon ni daga sakandire na wuce makarantar koyan aikin jiyya kai tsaye alhali wasu sai da suke je makarantun share fage kafin su sami gurbin karatun inji malama Amina Bello Suleman.

Malama Amina ta bayyana cewa an bata shawarar samun takardar tabbacin ita ‘yar asalin jihar kano ce wanda da hakan ya taimaka mata ta samun gurbin karatu a jihar.

Ta kara da cewa bayan kammala karatunta na aiki jinya, ta cigaba da karatun Unguwar Zoam, wato Midwifery, kuma bata fuskanci wata matsala ba illar mu’amala da marasa lafiya, wanda tun a makaranta aka koyar da su yadda zasu yi mu’amala da marasa lafiya.

Amina ta ce a matsayinta na ma’akaciyar jinya, an koya musu cewa marasa lafiya uzuri ake yi musu duba da irin lalurar da suke fama da ita a wannan lokaci, sannan a cewarta aiki yayi mata rana da rufin asiri a rayuwa.

Daga karshe ta ja hankalin matasa da su nemi ilimi ko ba don aiki ba domin su tarbiyantar da ‘ya’yansu a wannan zamani da ake ciki.

please wait

No media source currently available

0:00 0:05:36 0:00

  • 16x9 Image

    Ibrahim Jarmai

    Ibrahim Jarmai, ma’aikacin jarida (International Broadcaster Multi Media) a sashen Hausa na muryar Amurka, mai gabatar da shirye shirye a radio da talabijin, da kuma shafukan yanar gizo, dan asalin jihar Kasina.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG