Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Wani Dan Kasuwa Ya Shiga Hannun Hukuma


Wata kotu a Igbsere, jihar Legas, ranar Laraba ta yanke wa wani dan kasuwa mai shekaru 47 da haihuwa Maduabuci Onwuta, hukuncin daurin gidan yari har na shekaru 25 a sakamakon fyade da ya yi wa yarinya ‘yar watani 16 da haihuwa.

Mai shari’a Sedotan Ogunsanya, yayin da take gabatar da hukuncin, ta ce mai gabatar da kara ya yi bayani babu kokwanto akan wannan laifi.

Ta ce “na samu wanda ake zargi da laifin yi wa ‘yar yariyar fyade, kuma na yanke masa hukuncin daurin zama kurkuku har na tsawon shekaru 25, hukuncin zai fara aiki nan take daga ranar da aka yanke shi”.

A lokacin da ake sauraron karar, mai gabatar da karar ya bayyana cewa Mr Adebayo Haroun Maduabuci, ya aikata wannan laifi a ranar 23 ga watan Nuwambar shekarar 2013, a yankin Isheri.

Laifin fyade ya sabawa dokar laiffufuka ta Jihar Legas sashe na 137, wanda ya bukaci hukuncin kisa ko daurin rai da rai a gidan yari ga duk wanda aka samu da laifin.

  • 16x9 Image

    Ibrahim Jarmai

    Ibrahim Jarmai, ma’aikacin jarida (International Broadcaster Multi Media) a sashen Hausa na muryar Amurka, mai gabatar da shirye shirye a radio da talabijin, da kuma shafukan yanar gizo, dan asalin jihar Kasina.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG