Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Jajircewa Na Taimakawa Mutum Cimma Burin Sa Na Rayuwa -Inji Khadija Aliyu


Khadija Aliyu
Khadija Aliyu

Na kasance mace ta farko da ta fara shirin siyasa a gidan radiyon da nake aiki duk kuwa da kallon gazawa da ake yi wa mata inji malama Khadija Aliyu.

Khadija ta ce ta nemi gurbin karatu na aikin likitanci ko zama malamar jinya amma hakarta bata cimma ruwa ba, domin bayan ta rubuta jarabawar shiga jami’a wato Jamb, bata sami nasara ba, amma ta sake gwadawa inda daga bisani ta sauya sheka inda ta sami gurbin karatu na aikin jarida.

Ta ce bayan samun aikin jarida ta zama mace ta farko da ta fara shirin ‘yan siyasa a inda ta sami aiki, duk kuwa da abokan aiki da dama na ikrarin cewar ba zata iya rike shirin ba.

Khadija ta ce kafin ta fara fuskantar kalubale a harkar aiki a jami’a ma ta fuskanci wasu kalubalen mussamam ma kasancewar ta cikin makaranta ne ta yi aure har ta haihu kafinta kammala karatunta na jami’a.

Khadija ta ce ko da kuwa ba abinda ran mutu ke so ba jajircewa na taimakawa mutum wajen cimma burinsa da nunawa al’umma babu abinda mutum ba zai iya ba muddin ya sa a ransa zai iya.

Ta dai ja hankali matasa da su maida hankali wajen neman ilimi domin a cewarta rayuwa ta canza sai da neman ilimi.

please wait

No media source currently available

0:00 0:07:35 0:00

  • 16x9 Image

    Ibrahim Jarmai

    Ibrahim Jarmai, ma’aikacin jarida (International Broadcaster Multi Media) a sashen Hausa na muryar Amurka, mai gabatar da shirye shirye a radio da talabijin, da kuma shafukan yanar gizo, dan asalin jihar Kasina.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG