Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Matasa A Mayar Da Hankali Wajan Neman Na Kai - Inji Bilkisu Mai Sana'ar Hannu


Na fara sana’ar hannu ne kasancewar ban sami gurbin karatu ba a makarantar gaba da sakandare ba domin zama mai dogaro da kai inji Bilkisu Isah, matashiya mai sa’ar hannu.

Bilkisu ta bayyanawa DandalinVOA haka ne a yayin da take hira da wakiliyarmu Baraka Bashir, inda ta bayyana cewa jarabawarta bata yi kyau ba hakan ne ya sa ta fi maida hankali wajen zama mai dogaro da kai.

Da take ci gaba da bayani, matashiyar ta kara da cewa tun kafin ta kammala makarantar sakandire ta fara sayar da kayan yara, don karewa kanta takaicin zaman duniya, domin kaucewa fadawa yanayin rayuwa rayuwa.

Bilkisu, ta ce bayan sana’ar hannu tana koyon dinki a yayin da take dakon samun gurbin karatun boko.

Daga karshe ta ja hankalin ‘yan uwanta matasa da su mai da hankali wajen neman nasu na kansu sannan su maida hankali wajen karatun boko domin magance matsalolin yau da kullum.

please wait

No media source currently available

0:00 0:04:25 0:00

  • 16x9 Image

    Ibrahim Jarmai

    Ibrahim Jarmai, ma’aikacin jarida (International Broadcaster Multi Media) a sashen Hausa na muryar Amurka, mai gabatar da shirye shirye a radio da talabijin, da kuma shafukan yanar gizo, dan asalin jihar Kasina.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG