Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Southampton Ta Kori Kocinta Mauricio Pellegrino


A yayin da ya rage saura makonni takwas a kammala gasar Firimiya lig ta kasar Ingila, kungiyar kwallon Kafa ta Southampton, ta kori kocinta Mauricio Pellegrino.

Kungiyar ta ce ta sallame shi ne sakamakon rashin tabuka abin kirki a kungiyar musamman a gasar Firimiya lig.

Pellegrino dan shekaru 46 da haihuwa ya kama aiki a kungiyarne a watan yunin 2017 bayan ta Sallami kocinta Claude Puel, a sakamakon shima bai tabuka abin kirki ba.

Southampton, ta sami nasara a wasa daya ne kacal a cikin goma sha bakwai da ta yi a karkashin jagorancin Pellegrino, inda a ranar asabar da ta gabata Newcastle, ta lallasata da ci 3-0 a gasar Firimiya lig mako na 30.

A yanzu haka tana mataki na 17 da maki 28 a wasannin mako na 30 da ta buga na Firimiya lig. Kungiyar ta ce kafin ta yi wasanta da Wigan a ranar lahadi zata samo Kocin da zai cigaba da jagoranci kungiyar.

please wait

No media source currently available

0:00 0:04:23 0:00

  • 16x9 Image

    Ibrahim Jarmai

    Ibrahim Jarmai, ma’aikacin jarida (International Broadcaster Multi Media) a sashen Hausa na muryar Amurka, mai gabatar da shirye shirye a radio da talabijin, da kuma shafukan yanar gizo, dan asalin jihar Kasina.

  • 16x9 Image

    Bala Branco

    Bala Branco ma'aikacin jarida ne a Albarka Radio FM Bauchi dake tarayyan Najeriya wanda yake shirya wa Dandalin VOA labaran wasanni, Haifaffen Unguwar Nufawa ne dake birnin Bauchi. Mazaunin Bauchi a Najeriya.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG