Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugaba Barack Obama da 'yan Kungiyar Daular Islama


lISIS
lISIS

Shugaba Barack Obama ya ce zai fi mai da hankali kan mayar da hannu agogo baya ga 'yan kungiyar Daular Islama, game da nasarorin da su ka yi a Iraki.

Shugaba Obama ya yi maganar ce da manema labarai a Fadar White House a jiya Alhamis, dab da fara ganawa da tawagar manyan jami'ai na bangaren tsaro don tattauna rikicin Iraki da Syria.

Mr. Obama ya ce Amurka za ta cigaba da kai hare-hare kan wasu takamaimun wurare na Daular Islama a Iraki, ya na mai cewa wannan matakin ya raba mayakan sa kan da makamansu da kuma sauran kayan aikinsu.

To amma Shugaba Obama ya ce bayan wannan bai da wata dabara a kasa ta tinkarar mayakan sa kan a halin yanzu, sabanin cewa da ake ta yi wai ana gab da kai hari kan 'yan Daular Islama a Syria.

Shugaba Obama ya ce 'yan Daular ta Islama sun sami mafaka a Syria, kuma sojojin na Syria ba su iya zuwa wuraren da ke karkashin ikonsu.

XS
SM
MD
LG