Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ra'ayoyin Wasu Mawaka Kan Kalaman Ministan Sadarwa Da Al’adu


A wannan mako ne ministan sadarwa da al’adu, Lai Mohammad ya bada shawarar cewa gwamnatin Nijeriya ta hana mawaka da masu shirya fina-finai fita kasashen wajen domin gudanar da aikin daukar videon su a can.

Wannan batu dai ya bar baya da kura domin mawaka da dama ne ke yi wa wannan yunkurin na Lai mohammad kallon wata hanyar zagon kasa ga kasuwancin su.

A ta bakin Lai Muhammad, dai a cikin kundin tsarin aikin daukar fina-finai game da wakoki bai hallarta a fita wajen wata kasa ba, a cewarsa hakan na tauye ingancin kamfanoni da harkar daukar fin finai t Nijeriya.

A kan haka ne muka zanta da wasu daga cikin mawakan inda suke bayyana ra’ayoyinsu kamar daban daban

Saurari cikkakiyar hirar a nan.

please wait

No media source currently available

0:00 0:05:20 0:00

  • 16x9 Image

    Ibrahim Jarmai

    Ibrahim Jarmai, ma’aikacin jarida (International Broadcaster Multi Media) a sashen Hausa na muryar Amurka, mai gabatar da shirye shirye a radio da talabijin, da kuma shafukan yanar gizo, dan asalin jihar Kasina.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG