Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Mata Na Fuskantar Kalubale Wajen Neman Aikin Yi - Aisha


Matasa a sasan duniya da dama kan yi korafi kan irin wahalhalunda suke fuskanta wajen neman ayyukan yi idan sun kammala karatunsu.

Aisha Sani Aliyu, matashiya da ta karanci harshen Turanci da addini a Kano, ta ce ta yi karatu ne domin ta taimakawa al'ummarta mussaman ma mata tare da huce wa kai takaicin bani-bani.

Ta ce, duk da cewa ta yi karatu, tana sana’ar dogaro da kai kafin lokacin da za ta samu aikin gwamnati ko wani aiki na zuwa ofis.

Malama Aisha ta ce takan samu odar yin kayan tande-tande daga wajen abokai da kawayen arziki, mussaman a lokutan biki ko wani sha’ani.

Aisha ta ce, a yanzu abin da ke ci wa mata tuwo a kwarya bai wuce yadda mata ke fuskantar matsalar samun aiki bayan sun kammala karatu.

Daga karshe ta ce tana shawartar mata da su nemi ilimi, domin neman ilimi, ba’a girma da shi, tana mai cewa komai girman mace za ta iya fita ta yi karatu domin ta fadakar da al'ummarta.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:49 0:00

  • 16x9 Image

    Mahmud Lalo

    Dan jarida ne da ke aiki a Sashen Hausa na Muryar Amurka (VOA) a birnin Washington, DC na Amurka. Yana da kwarewa a rassa daban-daban na kafafen yada labarai, kamar wajen hada rahoto a takadar/mujallar jarida, fannin talbijin, rediyo, yanar gizo da kafafen sada zumunta na zamani, inda ya fi mayar da hankali kan batutuwan da suka shafi shugabanci na gari, ayyukan dogaro da kai, kiwon lafiya da kuma muhalli.

  • 16x9 Image

    Daula Saleem

    Daula Saleem, Ma’aikaciyar Jarida ce (International Broadcaster - Multimedia) a Sashen Hausa na Muryar Amurka dake birnin Washington, D.C. Yar asalin Jihar Katsina. Ta karanta aikin Jarida a Jami’ar Bayero University Kano.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG