Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Malaman Makaranta Sun Koka Akan Rashin Albashi


 'Yan Makaranta
'Yan Makaranta

Malaman makaranta ‘yan kwantragi bangaren kananan makarantu,a jamhuriyar Nijar, sun koka kan yadda har yanzu gwamnati bata biya su albashin su ba, wanda a cewar su rashin sa hannu ne ya kawo tsaikon.

Magatakarda na kungiyar, Malaman makaranta ‘yan kwantragi, Yau Abdu, yace wata biyu Kenan ba a biya Malaman makaranta ba saboda haka idan har gwamnati na bukatar a koma bakin aiki ba tare da tashin tashina ba toh ta gaggauta biya albashin.

Duk lokacin da matsala ta taso ana zama a tattauna tsakanin Malaman makarantar da mahukunta kuma ana samun fahimta a baya.

Malaman makarantar sun yi kira ga shuwagabanin dasu dauki maganarsu da mahimmaci gani cewa gwamnati a can baya tayi alkawarin daukar batun ilimi da mahimmanci.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:23 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG