Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kungiyar Enugu Rangers Ta Dakatar da Emetole


Hukumar gudanar war kwallon kafa ta ta Enugu Rangers ta bukaci babbabn kocin dinta Kelechi Emetole da ya kauce gefe guda na wani dan lokaci.

An cimma wannan shawarar ce a bayan wani taron gaggawa na kwanaki biyu da akayi a tsakanin hukumar gudanar war da kuma masu koyar da wasanni na kungiyar ta Ragers.

Sannan kuma an bukaci tsohon koci na fatakwal Sharks da Eyimba Imama Amapakoba wanda shima mai koyarwa ne a kungiyar ta Rangers da ya karbi ragamar babban kwac na wannan kungiyar na wani dan lokaci

Wata sanarwar da kungiyar ta bada a shafin super sport.com wadda ke dauke da sa hannun daraktan yada labarai Foster Chime, y ace wannan shawarar ta fara aiki daga jiya laraba wato 27 ga wata.

“an nada babban kocin Imama Amapakabo domin jan ragamar kungiyar har sai wani lokaci” a cewar chime.

kungiyar ta Enugu Rangers wadda sau 6 tana zamowa zakarar wasannin lig na Najeriya ita ce ta 12 daga cikin kungiyoyi 20 dake bugawa a gasar lig ta Firimiya ta Najeriya a bana, yayin da aka shiga mako na 10 da fara wasan a kakar kwallo ta bana.

XS
SM
MD
LG