Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kofin Duniya: Najeriya Za Ta Kece Raini Da Amurka a Poland


Wani wasa da Najeriya ke bugawa da kasar Ingila
Wani wasa da Najeriya ke bugawa da kasar Ingila

Ita dai Amurka za ta kara da Najeriya ne a daidai lokacin da take cikin fushin kayen da ta sha a hannun Ukraine.

Tawagar ‘yan wasan Najeriya ta Flying Eagles, za ta kece raini da ‘yan wasan Amurka, a ci gaba da gasar cin kofin duniya na ‘yan kasa da shekaru 20 da ke gudana a kasar Poland.

Za a buga wasan ne a birnin Bielsko- Biala, a wannan rukuni na D.

Gabanin wannan wasa, Eagles ta lallasa kasar Qatar da ci 4-0, yayin da ita kuma Amurka ta sha kaye a hannun Ukraine da ci 2-1.

Akwai yiwuwar wannan karawa ta zama mai sarkakiya ga 'yan wasan Najeriya, lura da cewa Amurka ba kanwar lasa ba ce.

Ita dai Amurka za ta kara da Najeriya ne a daidai lokacin da take cikin fushin kayen da ta sha a hannun Ukraine.

Ita kuma Najeriya za ta kara ne da burin ganin ta shiga rukuni na gaba, inda idan har ta yi nasara, za ta shiga zangon da-an-ci, an cire ka.

  • 16x9 Image

    Mahmud Lalo

    Dan jarida ne da ke aiki a Sashen Hausa na Muryar Amurka (VOA) a birnin Washington, DC na Amurka. Yana da kwarewa a rassa daban-daban na kafafen yada labarai, kamar wajen hada rahoto a takadar/mujallar jarida, fannin talbijin, rediyo, yanar gizo da kafafen sada zumunta na zamani, inda ya fi mayar da hankali kan batutuwan da suka shafi shugabanci na gari, ayyukan dogaro da kai, kiwon lafiya da kuma muhalli.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG