Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kannywood Na Fuskantar Barazanar Masu Satar Fasaha- Inji Umar UK


Umar UK
Umar UK

Kannywood na fuskantar barazana daga masu satar fasaha sakamakon bin matakin karshe na harkar kasuwancin fina-finai da masu shirya fina-finan da masana’antar Kannywood suka dauka inji mai shiryawa Umar Sani Kofar Mazugal wanda aka fi sani da Umar UK.

Umar ya bayyana haka ne yayin da yake zantawa da wakiliyar DandalinVOA Baraka Bashir inda ya ce a kasashen da aka cigaba masu harkar fim na fitar da fina-finan su ta hanyar bin matakan tallatawa da sayar da fina-finansu ta hanyar fitar da su a silma, sa’annan mataki na biyu a gidajen talabijin kafin ya fita ga jama’a.

Ya ce yin hakan na dakile masu satar fasaha samun damar sata har sai mai fim ya maida ribarsa, yana mai cewa, wadanda suka fara harkar fim yawanci shi’awa ce ta ja su, ba tare da sunyi la’akari da gudanar da bincike ba kafin a tsunduma ga harkar.

Umar ya ce matakan da kasashen waje ke bi sune ta amfani da gidajen kallo na silma, sannan gidajen talabijin inda ake basu hakkin su kamar yadda ya kamata, dan haka babu yadda za’ayi mai satar fasaha ya sata, sa’annan daga karshe bayan anbi wadannan matakai ne fim zai fita kasuwa.

please wait

No media source currently available

0:00 0:06:52 0:00

  • 16x9 Image

    Ibrahim Jarmai

    Ibrahim Jarmai, ma’aikacin jarida (International Broadcaster Multi Media) a sashen Hausa na muryar Amurka, mai gabatar da shirye shirye a radio da talabijin, da kuma shafukan yanar gizo, dan asalin jihar Kasina.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG