Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Idan Za'a Ci Gaba Da Biya Babu Wani Matsala In Ji Dalibai


Dalibai
Dalibai

Wakilan majalisar dokokin Nijar, sun kai wata ziyarar aiki jami’ar Damagaram, inda suka tattauna da daliban makarantar akan irin matsalolin dake ci masu tuwo a kwaya.

Sun kuma tabo batun tabarbarewar karabu a Damagaram, kamar yadda Sule Idi, mataimakin shugaban majalisar dokoki na hudu ya tabbatarwa muryar Amurka.

Bayan tattaunawa da dukkan wadanda abin ya shafa ‘yan majalisar sunyi alkawarin ganin cewa anyi sulhu.

A nasu bankaren daliban ta bakin shugaban kungiyar daliban jami’ar, Adam Ali Ali, yace tawagar wakilan sun nemi a yarjejeniya, yace sun amince amma idan za’a biya alwus alwus din dalibai kuma a ci gaba da biya ba wata matsala.

‘Yan majalisar sun yi kira ga Gwamnati da ta daidaita dukkan lamarin da ya shafi ilimi a jihar Damagaram

Su kuwa iyayen yara cewa suka yi sun fi kowa gamsuwa da ziyarar da ‘yan majalisar suka kai jami’ar domin ganin da ido, fatar su a kawo karshen matsalar dalibai su ci gaba da karatu cikin kwanciyar hakali

XS
SM
MD
LG