Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Gwagwarmayar Tabbatar Da Gwamnati Ta Bi Ka’idojin Kare Al’umma - Fatima M Umar


Fatima M Umar
Fatima M Umar

Dandalinvoa ya sami zantawa da wata ‘yar gwargwarmaya mai aiki da kungiyoyi masu zaman kansu ne wajen fafatukar kare muhalli da wata kungiya mai rajin kare ma’adanai da ke karkashin kasa tare da tabbatar da gwamnati ta bi ka’idojin kare al’ummar da ke yankin da ke fama da matsalolin da suka danganci kasa inji Fatima Muhammad Umar.

Har illa yau tana aiki da kungiyar da take kula da harkokin matasa da harkokin mata duk da zummar kare hakkin mata da matasa, kasancewarta mace ta ce rayuwa sai da gwagwarma domin ganin ba’a tauye hakkin mata ko matasa ba.

Ta ce kasancewar tana cikin wadannan kungiyoyi, tana fuskantar matsaloli da dama a cewar malama Fatima Umar, musamman ganin yadda samun aikin gwamnati a Najeriya said an wane da wane, dan haka dan haka zata ci gaba da gwagwarmaya.

Ta kara da cewa kasancewar samun ilimi da wayewa na zamani, a yanzu ko da ta fuskanci kalubale ba ta bari ya tauye ta ko ya hana ta aiki.

please wait

No media source currently available

0:00 0:04:04 0:00

  • 16x9 Image

    Ibrahim Jarmai

    Ibrahim Jarmai, ma’aikacin jarida (International Broadcaster Multi Media) a sashen Hausa na muryar Amurka, mai gabatar da shirye shirye a radio da talabijin, da kuma shafukan yanar gizo, dan asalin jihar Kasina.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG