Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Boko Haram Sun Gurgunta Wutar Lantarkin Jihohin Arewa Maso Gabas


Shekau da Mukarrabansa
Shekau da Mukarrabansa

Hare-haren ‘yan Boko Haram, ya tilastawa kamfanin samar da wutar lantarki, dake kula da jihohin Adamawa, Borno, Yobe da kuma Taraba rufe wasu ofisoshin kamfanin, a arewa maso gabashin Najeriya.

Hakkan ya jawo matsalar wutar lantarki, a wadannan jihohi, da yake karin haske dagane da wannan batu, jami’in hurda da jama’a, na kamfanin Alhaji Aliyu Hassan Ardo, yace kamfanin a yanzu, yana fama da karanci kudaden shiga.

Bayan matsalar samar da wutar lantarki, hare-haren na Boko Haram ya durkusarda harkokin kasuwancin a wadannan jihohi, inda a bangare guda hedkwatar tsaron Najeriya ta rufe wasu iyakokin kasar da kasar Kamaru, wanda a baya kuwa akan samu hada-hadan kasuwanci tsakanin al-umar kasacen biyu.

Boko Haram - 3'28"
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:28 0:00

XS
SM
MD
LG