Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Arsenal Ta Amince Da Tayin Fam Miliyan 4.45 Kan Lucas Perez


Kungiyar kwallon kafa ta Everton, ta cimma yarjejeniya da kungiyar Barcelona, kan sayen dan wasan bayanta Yerry Mina, mai shekaru 23 da haihuwa akan kudi fam miliyan 28.5 na tsawon shekaru biyar.

Har ila yau Kungiyar ta Everton, ta shaida wa Manchester united, cewa tana bukatar dan wasan bayanta Chris Smalling, ko kuma Victor Lindelof, dan shekaru 24, a duniya in har kungiyoyin biyu basu daidaita kan sayen dan wasan Manchester united ba.

Manchester United, na cigaba da shirye shiryenta na neman dan wasan Leicester, Harry Maguire mai shekaru 25, da tunanin kuma cewa za su biya kulob din kudi mafi yawa kan na kasar Ingila.

Chelsea na da sha'awar sayen dan wasan Crystal Palace, dan kasar Ivory Coast, Wilfried Zaha, mai shekaru 25, bayan Tottenham ta fita daga zawarcin sa, Sabon Kocin kungiyar Chelsea, Sarri yace kungiyar a shirye take ta sayar da mai tsaron ragarta Courtious, ga kungiyar Real madrid in har yana bukata.

Wakilin dan wasan tsakiya na Arsenal, Aaron Ramsey's ya musanta rade radin da ake yi na cewar dan wasan yace sai an bashi kudi fam dubu 300 a sati in har ana son ya sake sabunta kwantirakinsa a kungiyar, dan wasan dai yana da sauran yarjejeniyar kwantirakin shekara guda a kungiyar.

Arsenal ta amince da tayin fam miliyan 4.45 daga kungiyar Sporting Lisbon domin sayar da dan wasanta Lucas Perez mai shekara 29

Mousa Dembele, dan kasar Belgium mai shekaru 31 ya ki amincewa da tayin da aka yi masa na komawa kungiyar Inter Milan daga Tottenham.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:07 0:00

  • 16x9 Image

    Ibrahim Jarmai

    Ibrahim Jarmai, ma’aikacin jarida (International Broadcaster Multi Media) a sashen Hausa na muryar Amurka, mai gabatar da shirye shirye a radio da talabijin, da kuma shafukan yanar gizo, dan asalin jihar Kasina.

  • 16x9 Image

    Bala Branco

    Bala Branco ma'aikacin jarida ne a Albarka Radio FM Bauchi dake tarayyan Najeriya wanda yake shirya wa Dandalin VOA labaran wasanni, Haifaffen Unguwar Nufawa ne dake birnin Bauchi. Mazaunin Bauchi a Najeriya.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG