Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Cafke Wani Jami'an Kwastan da Tagwayen Jarirai


Rundunar ‘Yan Sandan jihar Ogun, ta cafke wani jami’in Kwastan Azeez, da matarsa a bisa zargin sun saye tagwayen jarirai akan kudi Naira 500,000, a Sango Otta dake cikin jihar Ogun.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa Azeez, wa amsa laifinsa yana mai cewa ya saye tagwayen ne baya da matarsa ta kasa haihuwa a karo na biyu bayan sun kwashe shekaru 23, da haihuwar farko.

Wandannan jarirai dai kwanakinsu hudu a duniya, kafin Azeez, da matarsa su amso su baya da suka biya Naira 500,000, tuni aka tasa keyar Azeez, da matarsa zuwa ofishin ‘yan Sanda, bangare masu liken asiri na CID dake Eleweran, a Abeokuta.

Da yake tabbatar da labarin kakakin ‘yan Sandan jihar ASP, Abimbola Oyeyemi, ya ce bangare masu kula da lamarin fataucin mutane na rundunar ‘yan Sandan ne ke ci gaba da binciken lamari.

XS
SM
MD
LG