Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Tsama Tsakanin Pep Guardiola Da Jose Mourinho


Mourinho and Guardiola
Mourinho and Guardiola

Sabon manajan kungiyar kwallon kafa ta Manchester City, Pep Guardiola, yayi watsi da hasashen da wasu masana tamaula keyi cewa wata sabuwar tsamar zata kunno kai a tsakaninsa da Jose Mourinho, wanda shi ma a kakar kwallo ta bana ya zamo sabon manajan daya kungiyar kwallon ta Manchester, watau United.

Masana tamaula sun ce manajojin biyu zasu sake sabunta wannan tsama ta su a fagen Firimiya Lig ta Ingila, a bayan da suka yi ta tsama a baya a kasar Spain, lokacin Guardiola yana koyar da FC Barcelona shi kuma Mourinho yana koyar da Real Madrid.

A jawabinsa na farko gaban ‘yan jarida tun bayan nada shi manajan Manchester City, Guardiola yace, “Ai Jose ya bayyana wannan lamarin daidai a lokacin da yace wannan lamarin fa ba wai a kansa ne ko a kai na ba.”

Ya ci gaba da cewa, “daga nesa abinda na hango shine cewa yana da wuya mutum ya lashe Wasanni a wannan lig na Firimiya.”

Da aka tambaye shi ko kungiyoyi nawa suka yi zawarcinsa daga Ingila, sai yace, “wannan kungiyar ce kawai don haka a koyaushe ina godiya sosai ga mutanen da suka amince da ni suka damka mini amana don in taho wannan kasa in koyar a Firimiya Lig.”

Yace ko ba dade ko ba jima, tilas ne kwach ya nuna irin kwazonsa a wasannin Firimiya Lig. Manchester City ta ba ni wannan dama kuma a koyaushe zan kasasnce mai godiya. Zan yi bakin kokari na domin in ga mun cimma gurorinmu, in ji Guardiola.

please wait

No media source currently available

0:00 0:01:37 0:00

XS
SM
MD
LG