Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugaban Kasar Liberiya George Weah Zai Karrama Arsène Wenger


Shugaban kasar Liberiya George Weah, yayi shiri domin karrama tsohon kocinsa, Arsène Wenger, da lambar yabo mai daraja a kasar.

Wenger ne ya sayi Shugaba George Weah, a lokacin da yake taka leda wanda ya kasance shi ne kadai dan wasan kwallon kafa daga Afirka da ya lashe kyautar dan kwallon duniya, a shekarar 1988, lokacin Wenger yana kocin kungiyar Monac,o dake kasar Faransa.

Koc Wenger, wanda a kwananne ya ajiye aikinsa a kungiyar Arsenal, bayan ya shafe shekaru 22 a matsayin koci, a yayin da yake Kocin ya sayi 'yan wasan Afirka da dama da suka buga wasa a karkashin sa.

Shi kuwa George Weah, ya yi ritaya daga buga wasan kwallon kafa a shekara ta 2003 inda ya fada cikin harkokin siyasa. Ya samu nasarar lashe zaben da a ka yi a Liberiya, a shekarar da ta gabata da gagarumin rinjaye.

A yayin hirarsa da manema labarai, ministan watsa labarai na kasar Liberiya, Eugene Nagbe, ya shaida wa manema labarai cewa ana sa ran Wenger, zai isa Monrovia, babban birnin kasar a ranar Asabar domin karbar lambar yabo daga shugaban kasar Laberiyan George Weah.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:10 0:00

  • 16x9 Image

    Ibrahim Jarmai

    Ibrahim Jarmai, ma’aikacin jarida (International Broadcaster Multi Media) a sashen Hausa na muryar Amurka, mai gabatar da shirye shirye a radio da talabijin, da kuma shafukan yanar gizo, dan asalin jihar Kasina.

  • 16x9 Image

    Bala Branco

    Bala Branco ma'aikacin jarida ne a Albarka Radio FM Bauchi dake tarayyan Najeriya wanda yake shirya wa Dandalin VOA labaran wasanni, Haifaffen Unguwar Nufawa ne dake birnin Bauchi. Mazaunin Bauchi a Najeriya.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG