Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Italiya Ta Dakatar Da Douglas Costa


Hukumar kwallon kafa ta kasar Itali ta dakatar da Douglas Costa, dan wasan kungiyar Juventus a wasanni hudu na Serie A, bayan wasansu da Sassuolo , a ranar Lahadi inda ta doke ta daci 2-1.

An sallami dan wasan dan kasar Brazil, mai shekaru 28, da haihuwa yayin wasan inda aka bashi Jan kati bayan da mataimakin alkalin wasa na VAR ya bayyanashi a TV karara yana tofa yawu a fuskar dan wasan Saussolo mai suna Federico Di Francesco.

Don haka bazai buga wasa da kungiyarsa zata yi da kungiyar Frosinone, Bologna, Napoli da kuma Udinese ba. Amman zai fafata a wasan da kulob din zai yi yau laraba a gasar zakarun nahiyar turai tsakaninta da Valencia.

Sai dai bayan tashi daga wasan Douglas Coast ya nemi afuwa daga wajan jagororin kungiyar da kuma magoya bayanta kan abun da tayi, sai dai hakan bai hana a hukunta shi ba.

Manchester City, ta ce ba ta riga ta fara tattaunawa da dan wasanta mai shekaru 23 a duniya ba mai suna Raheem Sterling ba, amma yanzu suna son yin tattaunawa akan mika tayinsu na yarjejeniyar da zata ƙare a shekara ta 2020.

An ambaci tsohon firaministan kasar Ingila Tony Blair a matsayin mai yiwuwa na gaba gaba cikin wadanda zasu zamo shugaba a bangaren gasar Premier League a wata tattaunawar da aka yi a cikin kwanan nan da kulob kulob masu buga gasar.

tsohon dan wasan Manchester United Dimitar Berbatov ya ce ya yi imanin cewa Juventus za iya kaiwa wasan karshe tsakanita da Manchester City ko Barcelona a gasar cin kofin zakarun Turai na bana.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:20 0:00

  • 16x9 Image

    Ibrahim Jarmai

    Ibrahim Jarmai, ma’aikacin jarida (International Broadcaster Multi Media) a sashen Hausa na muryar Amurka, mai gabatar da shirye shirye a radio da talabijin, da kuma shafukan yanar gizo, dan asalin jihar Kasina.

  • 16x9 Image

    Bala Branco

    Bala Branco ma'aikacin jarida ne a Albarka Radio FM Bauchi dake tarayyan Najeriya wanda yake shirya wa Dandalin VOA labaran wasanni, Haifaffen Unguwar Nufawa ne dake birnin Bauchi. Mazaunin Bauchi a Najeriya.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG