Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Akwai Bukatar Masu Hannu Da Shuni Da Gwamnatoci Su Shiga Harkar Waka- Ragaa


Akwai bukatar masu hannu da shuni da gwamnatoci su shigo cikin harkar wakokin mawakan Hausa, don inganta masana'antar wajen samar da kudaden shiga inji mai wakar hip-hop Musa Ragaa.

Ya bayyana haka ne a yayin da yake zantawa da wakiliyar DandalinVOA Baraka Bashir a garin Kanon Dabo.

Musa Ragaa ya ce babban abinda da ke ci wa matasan mawaka tuwo a kwarya bai wuce yadda ake yi wa harkar rikon sakainar kashi ba, ba'a baiwa harkar muhimmanci.

Ragaa ya ce a mafi yawan lokutan ana kallon mawaka a matsayin marasa tarbiya da da'a maimakon wasu mutane da ke inganata harshen Hausa tare da fadakarwa da nishadatarwa a lokaci daya

Ya ce baban burin sa ya bar baya ko da baya duk wanda ya ji wakar sa zai amfana ya kuma cewar Ragaa ya bar wa'azi a wakokinsa.

please wait

No media source currently available

0:00 0:05:46 0:00

  • 16x9 Image

    Ibrahim Jarmai

    Ibrahim Jarmai, ma’aikacin jarida (International Broadcaster Multi Media) a sashen Hausa na muryar Amurka, mai gabatar da shirye shirye a radio da talabijin, da kuma shafukan yanar gizo, dan asalin jihar Kasina.

XS
SM
MD
LG