Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Sa'ida: Nakan Aika Da Sakonni Masu Yawa, Ta Hanyar Waka Ga Jama'a


Sa'ida Adamu
Sa'ida Adamu

Lokaci yayi da mata matasa zasu canza tunaninsu, musamman na al’amuran da suka shafi zaman aure da soyayya, domin samun al’umma mai inganci, a cewar shahararriyar mawakiyar Hausa da Faransanci Sa’ida Adam.

Matashiyar mawakiyar dai ta bayyana haka ne a yayin da take zantawa da DandalinVOA a yau. Saida Adam, matashiyar mawaki wacce ta fi raja’a a wakokin rayuwa da al’amuran da suka shafi harkokin mata.

Ta ce tana duba matsalolin rashin kamun kai, da rashin zaman gidan aure da yawan buri da mata matasa ke yi a yanzu. Sai ta kara da cewar, wakokinta sun fi gabatar da nasihohi ga mata, tare da jan hankali al'umma, dama iyaye su sani cewar hakkokin sun rataya a wuyansu na tarbiyartar da diya mata.

Mawakiya Sa’ida, dai na yin wakokinta ne da harshen Hausa da kuma Faransanci kasancewar an haife ta a kasar Nijar, ta kuma yi rayuwarta a kasar Cote D’Ivoire, inda ta kamala karantunta a can.

Ta kara da cewar, ta gamsu da sakonnin da take isarwa ga ‘yan uwa matasa, kuma tana da burin samun fice kamar ragowar mawaka, inda take cewa takan fito a wasu fina-finan Kannywood duk a yunkurin ilmantar da masu sauraro da kallo.

  • 16x9 Image

    Yusuf Harande

    Yusuf Aliyu Harande, dan jaridar sashen Hausa na gidan radiyon Muryar Amurka (VOA). Dan asalin Hiliya a karamar hukumar Tambuwal, jihar Sakkwato.

XS
SM
MD
LG