Gidauniyar Almajirai ta Najeriya ta kira taron shan ruwa ko buda-baki, inda ta gayyato almajirai da nufin a hadu da sauran jama'a a yi buda baki a wannan wata mai tsarki na Ramadan.
Shugaban Gidauniyar Almajirai ta Najeriya, Alhaji Yusuf Hassan, yace su na gudanar da irin wannan taron shan ruwa kowace shekara, ya kuma yi bayanin dalilansu.
Haka kuma ya kara da bayanin irin ayyukan da wannan Gidauniya take gudanarwa.