Yanzu hukumar SSS din ta fito da makamai, tana barazanar harbin fararen hula masu aniyar gudanar da zanga-zangar lumana.
Da yake nuna damuwarshi game da wannan mataki, shugaban hadakar kungiyoyin da suka shirya wannan zama da dirshen Komrade Ibrahim Garba Wala yace an riga an kama wasu mambobinsu mutum uku.
“Abun takaici shine, jami’an tsaro sun hana mu gudanar da wannan abu. Sun gayyace mu zuwa Ofis dinsu, wanda muka gani cewa tamkar dama ce wadda zamu yi aiki dasu, jami’an tsaro saboda samawa al-umma da mu da muka fito, samun tsaron da ya kamata,” inji Ibrahim Wala.